Home General Rundunar ‘Yan sanda ta Musanta Kai Hari Kotun Majistare a Jihar Imo

Rundunar ‘Yan sanda ta Musanta Kai Hari Kotun Majistare a Jihar Imo

Rundunar ‘yan sandan Nijeriya reshen jihar Imo da ke kudancin kasar, ta yi watsi da rahotannin da wasu kafafofin yada labarai a kasar ke cewa ‘yan bindiga sun kai hari kan kotun majistire a jihar tare da banka ma ta wuta.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwar da kakakin rundunar ya fitar, inda ya ce wannan labari bashi da tushe bare makama, ta kuma yi mamaki da samu labarin hakan.

Ya bayyana cewa wutar lantarki ce ta janyo tashin gobara a kotun Majistare din, an kuma yi nasarar kashe ta ba tare da bata lokaci ba bisa agajin jami’an kashe gobara da jami’an tsaro.

An kuma killace harabar kotun da baza jami’an tsaro domin tabbtar da babu wanda ya shiga ciki, an kuma fara gudanar da bincike domin gano bakin zaren.

Wannan dai na zuwa ne, a daidai lokacin da wasu mahara na daban suka kai farmaki kan wata al’umma cikin Enugu wanda yayi sanadin mutuwar mutane da dama.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp