Home General An Gano Gawarwakin mutane sama da 200 Bayan Gumurzun da akayi da...

An Gano Gawarwakin mutane sama da 200 Bayan Gumurzun da akayi da ‘yan bindiga a jihar Zamfara

An gano gawawwaki 213 da suka hada da ‘yan ta’adda da masu kai musu bayanai, kwanaki kadan da mummunar musayar wutar da aka yi tsakanin sojojin Najeriya da ‘yan bindigar a wasu yankunan jihar Zamfara.

PRNigeria ta rawaito, sojoji 10 na daga cikin wadanda suka mutu a lokacin da ‘yan bindigar suka fantsama garuruwan da ke kusa.

idan za’a iya tunawa a  ranar Litinin PRNigeria ta rawaito dakarun rundunar Operation Hadarin Daji sun yi nasara kan ‘yan bindigar a kauyen Malele da ke karamar hukumar Dansadau a jihar Zamfara.

Samame ta sama da sojojin sama na Najeriyar suka kai a ranar Asabar ya yi nasarar hallaka gwamman ‘yan fashin dajin ciki har da wasu manya daga cikinsu.

An samu karuwar hare-haren ‘yan ta’adda a jihar Zamfara, sakamakon yadda sojojin Najeriya ke fatattakarsu daga inda suke buya, samamen da aka kai garuruwan Malele, Maigoge, Yan Sawayu, Ruwan Tofa, Mai Awaki, and Zama Lafiya, da ke karkashin gundumar Mutunji a karamar hukumar Dansadau sun kara kai mi.

‘Yan fashin daji da masu garkuwa da mutane domin neman kudin fansa na ci gaba da zama babbar barazana a jihar Zamfara, inda suke haddasa rasa rayuka da dukiya, ko da yake gwamnatin jihar da jami’an tsaro na cewa su na bakin kokarin magance matsalar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp