Home General Sojojin Najeriya sun hallaka mayakan kungiyar boko haram 140 a cikin watan...

Sojojin Najeriya sun hallaka mayakan kungiyar boko haram 140 a cikin watan Disamban 2022

Sojojin Najeriya sun hallaka jimullar mayakan kungiyar boko haram kimanin 140 a cikin watan Disamban 2022.
An kashe adadin mutanen ne a hare-haren da aka kai tsakanin ranar daya zuwa 22 ga watan, sannan kuma an ji wa wasu da dama munanan raunuka.
A cewar Zagazola Makama, kwararre kuma mai sharhi kan al’amuran tsaro a yankin Tafkin Chadi, rundunar sojan kasa da na sama na Operation HADIN KAI sun ci gaba da mamaye yankin gaba daya na ayyukansu.
Ya ce an sami nasarar ce a kauyuka da garuruwa da tsaunuka da ke cikin Kananan Hukumomin Damboa, Bama, Gwoza da Konduga na jihar Borno, da kuma na Gulani da Geidam dake Jihar Yobe.
A cewar Zagazola, musamman a ranar 1 ga Disamba, 2022, sojoji sun gwabza da ’yan ta’addan Boko Haram dana tsagin ISWAP a Damboa ta jihar Borno.
Dakarun da ke samun goyon bayan jiragen sama sun yi artabu da ’yan ta’addan tare da kashe da dama yayin da sauran suka gudu da manyan raunuka a jikinsu.
Sojojin sun yi amfani da dabaru yaki inda suka kwato bindigogi kirar AK47 guda shida, bindigogin FN 3, bindigogin kirar QJC guda 2, alburusai 102 masu tsayin 12.7mm, 2,152 na musamman na 7.62mm na musamman, 20 masu tsayin 7.62mm NATO, bututu 1 RPG, bam 1 HEAP, 1 HEAP Bom.
Sauran makaman da aka kwato sun hada da bam da gurneti na hannu.
Sojojin sun kuma samu nasarar kwato daya daga cikin motar ’yan ta’addan tare da lalata wata motar bindiga guda daya.
Hakazalika, a ranar biyu ga Disamba, 2022, sojojin da ke sintiri na yaki sun yi karo da ‘yan ta’adda a yayin da suke yin amfani da dajin da ke wajen garin Mallam Fatori a Karamar Hukumar Abadam ta jihar Borno.
A yayin musayar wuta a wannan hari sojoji sun kashe ’yan ta’adda biyar tare da kama daya.
Har ila yau, a ranar 11 ga Disamba, 2022, sojoji sun kama kwamandojin ’yan ta’addar Boko Haram hudu a kan hanyar Gwoza zuwa Yamteke a Karamar Hukumar Gwoza ta jihar Borno.
An bayyana cewa sun tsere ne daga Sabil Huda da ke dajin Sambisa saboda tsananin ruwan bama-bamai da dakarun nasu suka yi.
Abubuwan da aka kwato daga hannun ’yan ta’adda sun hada da bindigogin AK-47 guda uku, bindiga korar G3 guda daya, da alburushi 20 na musamman na 7.62mm, harsashi guda 12 da wayoyin hannu guda biyu da tsabar kudi Naira 125,400 da sauran kayayyaki.Sojojin Najeriya sun hallaka jimullar mayakan kungiyar boko haram kimanin 140 a cikin watan Disamban 2022.
An kashe adadin mutanen ne a hare-haren da aka kai tsakanin ranar daya zuwa 22 ga watan, sannan kuma an ji wa wasu da dama munanan raunuka.
A cewar Zagazola Makama, kwararre kuma mai sharhi kan al’amuran tsaro a yankin Tafkin Chadi, rundunar sojan kasa da na sama na Operation HADIN KAI sun ci gaba da mamaye yankin gaba daya na ayyukansu.
Ya ce an sami nasarar ce a kauyuka da garuruwa da tsaunuka da ke cikin Kananan Hukumomin Damboa, Bama, Gwoza da Konduga na jihar Borno, da kuma na Gulani da Geidam dake Jihar Yobe.
A cewar Zagazola, musamman a ranar 1 ga Disamba, 2022, sojoji sun gwabza da ’yan ta’addan Boko Haram dana tsagin ISWAP a Damboa ta jihar Borno.
Dakarun da ke samun goyon bayan jiragen sama sun yi artabu da ’yan ta’addan tare da kashe da dama yayin da sauran suka gudu da manyan raunuka a jikinsu.
Sojojin sun yi amfani da dabaru yaki inda suka kwato bindigogi kirar AK47 guda shida, bindigogin FN 3, bindigogin kirar QJC guda 2, alburusai 102 masu tsayin 12.7mm, 2,152 na musamman na 7.62mm na musamman, 20 masu tsayin 7.62mm NATO, bututu 1 RPG, bam 1 HEAP, 1 HEAP Bom.
Sauran makaman da aka kwato sun hada da bam da gurneti na hannu.
Sojojin sun kuma samu nasarar kwato daya daga cikin motar ’yan ta’addan tare da lalata wata motar bindiga guda daya.
Hakazalika, a ranar biyu ga Disamba, 2022, sojojin da ke sintiri na yaki sun yi karo da ‘yan ta’adda a yayin da suke yin amfani da dajin da ke wajen garin Mallam Fatori a Karamar Hukumar Abadam ta jihar Borno.
A yayin musayar wuta a wannan hari sojoji sun kashe ’yan ta’adda biyar tare da kama daya.
Har ila yau, a ranar 11 ga Disamba, 2022, sojoji sun kama kwamandojin ’yan ta’addar Boko Haram hudu a kan hanyar Gwoza zuwa Yamteke a Karamar Hukumar Gwoza ta jihar Borno.
An bayyana cewa sun tsere ne daga Sabil Huda da ke dajin Sambisa saboda tsananin ruwan bama-bamai da dakarun nasu suka yi.
Abubuwan da aka kwato daga hannun ’yan ta’adda sun hada da bindigogin AK-47 guda uku, bindiga korar G3 guda daya, da alburushi 20 na musamman na 7.62mm, harsashi guda 12 da wayoyin hannu guda biyu da tsabar kudi Naira 125,400 da sauran kayayyaki.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp