Home General Mutum 8 Sun Mutu a rikicin kabilanci a Sudan

Mutum 8 Sun Mutu a rikicin kabilanci a Sudan

Jami’an agaji a yankin Darfur na ƙasar Sudan sun ce akalla mutane takwas ne suka mutu a rikicin da ya ɓarke a cikin dare tsakanin wasu al’ummomin da ke zaman doya da manja.

Da farko dai an fara harbe-harbe ne a garin Zalingei, daga bisani ‘yan kabilar Rizeigat ta Larabawa, da suka kai hari wani sansanin ‘yan gudun hijira na ‘yan kabilar Fur, a kan babura.

Ɓarkewar tashe-tashen hankula sun karu tun bayan janyewar tawagar wanzar da zaman lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya a bara.

Har yanzu dai yankin na Darfur bai farfaɗo ba daga yaƙin da ya sha fama da shi tun kusan shekaru ashirin da suka gabata, wanda ya raba sama da mutane miliyan biyu da gidajensu.

Ana zargin da sa hannun wasu mayakan sa kai da ke samun goyon bayan gwamnati a wasu hare-haren da ake kaiwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp