Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta miki ta’aziyyar ta bisa Rasuwar Pele

Shugaban Najeriya Muhammadu ya Buhari ya bi sahun shugabannin ƙasashen duniya wajen miƙa saƙon ta’aziyyarsa kan rasuwar fitaccen ɗan ƙwallon duniya Edson Arantes do Nascimento wanda aka fi sani da Pele.

A wata sanarwa da mataimaki na musamman ga shugaban ƙasar kan kafofin yaɗa labarai Malam Garba shehu ya fitar, shugaba Buhari ya bayyana ɗan wasan da cewa mutum ne ”mai kirki da ƙanƙan da-kai, duk da cewa shi babban ɗan wasa ne”.

”Pele ya gina kyakkyawar alaƙa tsakanin ƙasashe, da ƙabilu da ma addinai, haƙiƙa duniya ba za ta manta da shi ba”, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Tsohon gwarzon ɗan wasan duniyar ya mutu ne ranar alhamsi bayan ya sha fama da rashin lafiya.

Ya lashe kofin duniya uku tare da zura ƙwallaye sama da 1,281, ya zama zaƙaƙurin ɗan wasan duniya.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 11 hours 29 minutes 15 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 10 minutes 40 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com