Home General Rundunar sojojin Ruwan Nijeriya ta bukaci Jami’anta dasu kasance masu da’a da...

Rundunar sojojin Ruwan Nijeriya ta bukaci Jami’anta dasu kasance masu da’a da nuna kwarewa

Kwamandan Rindunar dake lura da yankin Abuja, Commodore Abdulrahman Muhammed, inda ya yabawa manyan Jami’an rundunar bisa kyawawan hali gami da kwarewa da yadda suke gudanar da ayyukan su cikin sadaukarwa.
Kwamandan ya bayyana hakan ne a wani biki mai lakabin Naval Unit Abuja Social Activities (NUASA 2022) wanda ke nuna an kawo karshen shekarar 2022.
Ya kuma bukace su dasu kara kaimi wajen sake firo da kimar rundunar ta sojin Ruwan Nijeriya.

Babban shugaban sashen Mulki na Shalkwatar rundunar Rear Admiral Barabutemegha Jason Gbassa wanda ya sami wakilcin Rear Admiral Kennedy Obi Egbuchulam, wanda shima ya bukaci jami’an dasu kasance masu sadaukar da kai, Da’a da kuma nuna gogewar aikin na soja ta hanyar kare lafiya da dokiyoyin Al’umma.
Yace “ina matukar yaba muku bisa rawar da kuka taka wajen samun nasarar rundunar Sojojin Ruwan Nijeriya. wannan ya samar da yanayi mai ga Al’ummar birnin Abuja masu kaunar zaman Lafiya domin gudanar da bikin Kirsimeti da sabuwar shekara.

Bikin na Naval Unit Abuja Social Activities (NUASA 2022) ya sami halartar iyaye, yara inda aka gudanar gasa kala-kala, wasan barkwanci, tambayoyi da amsa ga yara domin kara armashin taron.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp