Home General Mai Martaba sarkin katsina ya nada shugaban hukumar NIA matsayin Sardaunan Katsina.

Mai Martaba sarkin katsina ya nada shugaban hukumar NIA matsayin Sardaunan Katsina.

Mai Martaba sarkin katsina ya nada shugaban hukumar NIA Ahmed Rufa’I matsayin Sardaunan katsina.
An nada babban daraktan hukumar tattara bayanan sirri Amb. Ahmed Rufa’I Abubakar matsayin sardaunan Katsina.
Mai martaba sarkin katsina Alhaji Abdulmumin Kabir Usman ya nada shugaban hukumar ta NIA matsayin sardaunan na katsina a ranar Asabar.
Taron nadin sarautar ya sami halartar manyan jami’an Gwamnatin Nijeriya, cikin su har da shugaban majalisar Dattawan Nijeriya, Ahmed Lawan.
Amb. Ahmed Rufa’I ya fito daga zuri’ar Muhammad Maude, Jarumi kuma sadauki, wanda tarihi ya nuna shine wanda ya samar da Unguwar Maude dake katsina a cikin a kashin farko cikin ukun karni na 19.
An gudanar da nadin ne a fadar mai martaba sarkin katsina, cikin nutsuwa da annashuwa, taron ya sami halartar manyan baki daga ciki da wajen kasar.
Da yake jawabi ga dimin jama’a da suka sami halartar taron nadin mai martaba sarkin Katsina, yace nadin sarautar sardaunar da aka yiwa shugaban hukumar ta NIA, ya nuna godiya da irin kyakkyawar hidimar da ya yiwa katsina, nijeriya da kuma tsarin kasa da kasa, gami da jajircewa wajen aiki tukuru da rikon amana.
Sarkin yayi kira ga sauran masu rike da madafun iko a Nijeriya da su yi aiki da aminci tare da sauke nauyin dake kan su.
Sarkin ya bayyana kabilanci da nuna banbancin addinin matsayin abinda ke kawo tasgaro ga hadin kan kasa, inda ya bukaci ‘yan kasar dasu kawar da su domin samun cigaban kasar.
Sabon sardaunan katsina, Ahmad Rufa’I Abubakaya sami lambobin yabo da dama. Suka hadar da DGNIA bisa kwazo sai kuma lambar yabo ta l’Ordre National de la Republique du Niger wanda shugaban jamhuriyyar Nijar ya damka masa, sai kuma lambar yabo ta CFR, wadda shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya bashi, da dai sauran manyan lambobin girmamawa daya samu

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp