Home General Kwankwaso yace zai ingata fannin Ilimi idan ya zama shugaban Nijeriya

Kwankwaso yace zai ingata fannin Ilimi idan ya zama shugaban Nijeriya

Abuja – Dan takarar shugaban kasa a inuwar New Nigerian Peoples Party, Rabiu Kwankwaso, yace idan ya ci zabe, gwamnatinsa zata gina Azuzuwan karatu 500,000 ga yara kanana marasa galihu.

Kwankwaso ya dauki wannan alkawarin ne ranar Litinin a wurin kadammar da kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa, (PCC), a birnin tarayya Abuja.

Haka nan Kwankwaso ya bayyana cewa gwamnatinsa zata tabbata manyan makarantun gaba da Sakandire sun kai matakin gogayya a duniya.

Kwankwaso yace “Bari na tuna mana cewa a shirye muke mu sauya bangaren ilimi domin mu inganta shi kuma kowa ya samu damar neman ilimi. Musamman zamu gina Azuzuwa 500,000 a sassan jihohin kasar nan.”

“Zamu zuba kananan yara sama da miliyan 20m dake gararamba a sabbin Azuzuwa domin muna da kudirin kawar da su daga yawo a Titunan Najeriya. Zamu maida duk wani Fam na neman gurbi da ɗaukar aiki kyauta.”

“Jarabawar gama Sakandire da ta share fagen shiga manyan makarantu kamar WAEC, NECO, NABTEB, NBIAS, JAMB da sauransu zamu maida su kyauta ga ‘yan Najeriya.”

Da yake tabo Jami’a, kwalejin fasaha da sauran manyan makarantun gaba da sakandire, tsohon gwamnan jihar Kano ya ci gaba da cewa:

“Zamu inganta tare da fadada jami’oi, kwalejojin fasaha, da baki daya kwalejojin mu na ilimi kuma mu daga darajarsu su kai matakin gogayya a duniya. SH

NNPP ta kaddamar da shafin tallafawa kamfen Kwankwaso

Bayan haka, jam’iyyar NNPP mai kayan marmari ta kaddamar da bude shafin yanar gizo na hada kuɗi domin taimaka wa yakin neman zaben shugaban kasa.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp