Home General Mayakan ISWAP Sun mika wuya a Jamhuriyyar Nijar

Mayakan ISWAP Sun mika wuya a Jamhuriyyar Nijar

Mayajan kungiyar tada kayar Baya na ISWAP da suka tsallake rijiya da baya, bayab harin da tsagin Boko Haram ya kai mu a Kayowa da Toumbun Gini, a Arewa maso gabshin yankin Tafkin Chadi, sun mika wuya hannun hukumomi a Tumour, ta Jamhuriyyar Nijar.
Zagazola ya ruwaito cewa mayakan ISWAP sun mika wuya a ranar 10 ga watan Janairu biyo bayan harin da abokan hamayyar su ta boko haram ke kai musu.

Harin ISWAP kan sansanin boko haram ya haifar da asarar rayuka tun a ranakun 31 ga Disamba da kuma 8 ga watan Janairun, 2023.
Harin kungiyar ta kai bisa jagorancin ABU UMAIMAH da akafi sanj da BAKOURA DORO, ya tarwatsa maboyar yan Ta’addan dake Toumbum Allura, Kurnawa, Kayowa da kuma Toumbun Gini, wanda ya tilastawa Abu Moussab al-Barnawi da wasu kwamandojin tsirewa.

Ci gaba da fafatawa tsakanin JAS da ISWAP dai da alama dai ba mai karewa ba ce ganin yadda yunkurin da kungiyoyin ke yi na hada karfi da karfe domin yakar sojojin Najeriya da na MNJTF ya gagara.

Dangane da wannan yanayin ne kungiyar ISWAP ke neman goyon bayan mayakan ISIS na kasashen waje da suka hadar da Mali, Burkina Faso da Somaliya don taimaka musu su karya JAS.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp