Home General An sanya dokar hana fita a Jihar Niger

An sanya dokar hana fita a Jihar Niger

Gwamnatin jihar Niger ta sanya dokar ta baci biyo bayan kisan wani mai gari a jihar.
Gwamnan jihar Niger Abubakar Sani Bello ya sanay dokar hana zirga-zirga a kauyen
Lambata dake karamar hukumar Gurara, biyo bayan wata hatsaniya da tayi sanadiyyar hallaka wani mai rike da sarautar gargaji Mohammed Abdulsafur.
Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da sakataren Gwamnati jihar Ahmed Matane, ya fitar a ranar lahadi a Minna babban birnin jihar.
Rahotanni sun bayyana cewa ‘yan daba sun hallaka dagacin Lamabata ne a ranar Asabar biyo bayan wata tarzoma.
Bello ya bada umarnin cewa

Dokar zata fara ne daga karfe 6:00am Zuwa 6:oopm farawa daga ranar Lahadi kuma har sai baba ta gani.
Ya kara da cewa an sanya dokar ne domin taimakawa jami’an tsaro su nemo bakin zaren matsalar, su tseratar da Rayukan Al’umma da dawo da doka da Odar.
Sanarwa ta kuma bayyana cewa Gwamnatin jihar tayi Allawadai da wannan tarzoma data auku a garin na lambata.
Ta kuma bukaci Al’ummar garin dasu bi doka domin baya jami’an tsaro damar dawo da zaman lafiya a garin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp