Home General Zargin sayar da Man Fetur Ba bisa ka’ida ba ya haddasa Gobara...

Zargin sayar da Man Fetur Ba bisa ka’ida ba ya haddasa Gobara a Gidan Man NNPCL Na Jihar Kano

Zargin sayar da man fetur ba bisa ka’ida bay a haddasa tashin wata gobara a gidan mai mallakin kamfanin NNPCL dake shatale-talen kano Club dake jihar kano a Arewa maso yammacin Nijeriya.
Wannan dai iftila’I na zuwa ne daidai lokacin da Al’umma jihar da wasu jihohihin dake kasar ke fama da matsalar karanci da tsadar manfetur sakamakon rashin tartibin farashin sa.
Shaidun gani da ido sun tabbatar wa da PRNigeria cewa bayan kammala zuba man ne a wata mota kirar Sienna wadda aka yi mata Karin tanki ne lamarin ya auku.
Sai dai duk da kokarin hukumar kashe gobara na dakile yaduwar gobarar lamarin sai da ya kai ga konewar motar kurmus.
Wani shaida ma da lamarin ya faru gaban idon sa wanda ya bukaci a sakaye sunan  sa sakamakon alaka da yake da ita da gidan man yace, ana tsaka da zuba man ne hukumomin gidan man suka hangi hukumar tsaro ta farin kaya dake yawo domin ganin an sayar da man yadda yake a farashin da gwamnati ta bayar, nan ne a kokarin su na gaggauta boyewa wutar ta tashi a motar.

Ba wannan ne karon farko da gobara ke tashi a gidajen man dake jihar kano ba sai dai a iya cewa wannan yazo da sauki domin kawo yanzu babu wani rahoton asarar rayuka sakamakon gobarar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp