Dakarun sojojin Nijeriya sun tarwatsa maboyar yan Ta’addan a karamar hukumar Chikum.

Sojojin Rundunar Operation Forest Sanity inda suka tarwatsa ‘yan bindiga 2 tare da tarwatsa maboyar su a karamar hukumar chikum dake jihar kaduna.

Wannan na kunshe ta cikin wata da kwamishinan tsaro da al’amarun ciki na jihar Kaduna Samuel Aruwa.
Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da
Ta cikin wani rahoton bayan atisaye da Gwamnatin jihar ta samu ya bayyana cewa dakarun sun sami nasarar ne yayin wani bata kashi da sukayi Akan hanyar Kaboresha-Rijana dajin-Kuzo-Kujeni zuwa mashigar Gwanto zuwa Kachia.
Dakaru. Sun yi kwantan bauna akan hanyar Gwanto-Kwasau, inda su kuma ‘yan ta’addan suka nufi wajen haye bisa babura.
Sojojin sun sami natsara hallaka yan bindiga 2 tare da kwato babura 3.
Haka kuma dakarun sun sami nasarar tarwatsa maboyar dake kutura zuwa Rijana inda ‘yan Ta’addan suka afka cikin daji bayan sun hangi sojojin, inda aka sami babura 3 a wajen.

Haka kuma an sami damar kwato wasu abubuwan da suka hadar da kayan sojoji da wasu sauran kayayyakin yaki.
Gwamnatin jihar tace dakarun na cigaba da kai hare-haren kan ‘yan Ta’addan, ta bukaci Al’ummar jihar dasu cigaba da bada bayanan sirri.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 22 hours 45 minutes 4 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1173 days 26 minutes 29 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com