Home General Kabiru Sufi ya zama Dan Adalan masarautar Dambatta

Kabiru Sufi ya zama Dan Adalan masarautar Dambatta

Sarkin Fulanin Dambatta da ke jihar Kano, Alhaji Aminu Bello Sulaiman ya amince da naɗin Dr. Kabiru Sa’id Sufi a matsayin Dan Adalan ƙasar Dambatta.

Sanarwar naɗin na ƙunshe cikin wata sanarwa da fadar Sarkin Fulanin Dambatta ta fitar mai dauke da sa hannun shugaban kwamitin shirye – shirye Dr. Bello Adamu Namura.

Sanarwar ta ce “Bisa dogon nazarin halayenka da kuma la’akari da gudummawarka ga Dambatta, jihar Kano da kasa baki daya, da kuma girmama masarautar Dambatta, Mai girma Sarkin Fulani-Dambatta ya umarci a sanar dakai cewa kana daya gada cikin wadanda ya amince a baka mukamin sarautar DAN ADALA a kasar Dambatta

Saboda haka an tsara jadawalin shirye shirye da tsare tsaren bikin nadin, wanda da zajar an gama shirye shiryen bikin nadin sarautar, kwamitin tsare tsaren zasu sanar da kat lokacin da za’ayi bikin nadin da zarar an sa rana”

“A madadin Mai girma Sarkin Fulani, muna tayaka murnar samun warnan sarauta da kuma addu’ar Allah Ya tayaka riko, Ya zama jagora bisa wannan amana da nauyi daya dora maka. Muna kuma fatan za’a bada hadin kai wajen bin umurni da dokokin wannan masarauta”

Dakta Kabiru Sufi babban malami ne a kwalejin share fagen shiga jami’a da ke jihar Kano, mamba ne a ƙungiyoyi da dama a ciki da wajen Najeriya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp