Home General Jirgin Kasan Kaduna zuwa Abuja zai dawo aiki ranar talata

Jirgin Kasan Kaduna zuwa Abuja zai dawo aiki ranar talata

Hukumar Zirga-Zirgar Jiragen Kasa ta Najeriya (NRC) ta sanar da dawowar aiki jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna wanda aka dakatar sakamakon hatsari da ya yi a tashar Kubwa a makon da ya gabata, ranar Juma’a 27 ga watan Janairu, 2023.
NRC a cikin wata sanarwa, ta ambaci Daraktan Ayyuka, Injiniya Niyi Ali, na cewa jirgin zai dawo aiki a ranar Talata 31 ga Janairu 2023.
Jadawalin jirgin da aka fitar ya nuna jirgin farko daga Kaduna zuwa Abuja zai tashi da karfe 7 na safe yayin da jirgin farko daga Abuja zuwa Kaduna zai tashi da karfe 10 na safe.
Jirgi na biyu daga Kaduna zai tashi da karfe 1:00 na rana, yayin da jirgin Abuja zuwa Kaduna zai tashi da karfe 4 na yamma.
Sai dai a ranar Laraba jirgin kasa daya ne zai tashi daga Kaduna zuwa Abuja da misalin karfe 7 na safe sai kuma wanda zai tashi daga Abuja zuwa Kaduna da misalin karfe 4 na yamma.
“Muna nadamar duk wata matsala da fasinjojinmu masu suka fuskanta sakamakon matsala da jirgi ya samu ya samu.”

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Manyan Tsofaffin Jami'an Soji 10 da Suka Rasa Rayukansu a Hannun ƴan Ta'addaTarihin Rayuwar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaMatsalar Tsaro: Masu Zanga-Zanga Sun Tare Babbar Hanyar AbujaDuk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da 'Yan Ta'adda, za a ɗauke shi a Matsayin ɗan ta’adda - Christopher MusaFarashin ɗanyen Mai ya Faɗi Bayan Amurka ta Soke Sabbin Hare-Haren kaiwa IranAmurka ta yi sulhu kan yaƙin da ta ke yi da Iran - TrumpMajalisar Wakilan Najeriya ta Amince da ƙudirin Dokar Kafa ’Yan sandan JihaHukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar NejaMiyagun ƙwayoyi da Makamai: Jami'an Tsaro Sun Kama Mutane 8 a Jihar YobeAbin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a Sokoto
X whatsapp