Home General NNPC na neman kariyar sojoji domin fara hako man fetur a Borno

NNPC na neman kariyar sojoji domin fara hako man fetur a Borno

Kamfanin Man NNPC a Najeriya ya nemi taimakon rundunar soji ta 7 da ke da cibiya a Maiduguri da ta taimaka masa wajen bai wa ma’aikatan da za su yi aikin hako mai a gabar Tafkin Chadi kariyar da ake bukata.

Manjo Janar Ali Nani mai ritaya, ya jagoranci tawagar wasu mutane 3 domin ganawa da kwamandan runduna ta 7, Manjo Janar Waidi Shuaibu domin gabatar da bukatar da kuma tattaunawa kan yadda za a samu biyan bukata.

Sanarwar da kakakin rundunar ya gabatar, ta ce Janar Nani ya gabatar da bukatar ce a madadin kamfanin Didan wanda NNPC ya ba shi aikin hako man.

Kwamandan runduna ta 7 Janar Shuaibu ya yi alkawarin bai wa ma’aikatan tsaron da suke bukata domin gudanar da ayyukansu.

Janar Shuaibu ya ce rundunar za ta ci gaba da bada gudumawar da ta dace wajen kare lafiyar ma’aikatan da kuma kayan aikinsu, yayin da ake aikin sake gina yankin da rikicin Boko Haram ya shafa.

A shekarun baya, irin wannan yunkuri na kamfanin man ya gamu da koma baya lokacin da mayakan Boko Haram suka kama wasu daga cikin ma’aikatan da ke aiki a yankin.

Masana ma’adinai sun dade suna danganta Jihar Borno, musamman yankin Tafkin Chadi da arzikin man fetur da kuma iskar gas.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp