Home General NNPC na neman kariyar sojoji domin fara hako man fetur a Borno

NNPC na neman kariyar sojoji domin fara hako man fetur a Borno

Kamfanin Man NNPC a Najeriya ya nemi taimakon rundunar soji ta 7 da ke da cibiya a Maiduguri da ta taimaka masa wajen bai wa ma’aikatan da za su yi aikin hako mai a gabar Tafkin Chadi kariyar da ake bukata.

Manjo Janar Ali Nani mai ritaya, ya jagoranci tawagar wasu mutane 3 domin ganawa da kwamandan runduna ta 7, Manjo Janar Waidi Shuaibu domin gabatar da bukatar da kuma tattaunawa kan yadda za a samu biyan bukata.

Sanarwar da kakakin rundunar ya gabatar, ta ce Janar Nani ya gabatar da bukatar ce a madadin kamfanin Didan wanda NNPC ya ba shi aikin hako man.

Kwamandan runduna ta 7 Janar Shuaibu ya yi alkawarin bai wa ma’aikatan tsaron da suke bukata domin gudanar da ayyukansu.

Janar Shuaibu ya ce rundunar za ta ci gaba da bada gudumawar da ta dace wajen kare lafiyar ma’aikatan da kuma kayan aikinsu, yayin da ake aikin sake gina yankin da rikicin Boko Haram ya shafa.

A shekarun baya, irin wannan yunkuri na kamfanin man ya gamu da koma baya lokacin da mayakan Boko Haram suka kama wasu daga cikin ma’aikatan da ke aiki a yankin.

Masana ma’adinai sun dade suna danganta Jihar Borno, musamman yankin Tafkin Chadi da arzikin man fetur da kuma iskar gas.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp