Home General Buhari – Nan da kwanaki 7 zamu magance matsalar Kudi a Nijeriya

Buhari – Nan da kwanaki 7 zamu magance matsalar Kudi a Nijeriya

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bukaci yan kasar da su ba shi kwanaki bakwai kacal domin magance matsalolin kuɗi da ake fuskanta a kasar.

Shugaban ya bayyana haka ne a wani taro da ya yi da ƙungiyar gwamnonin Jam’iyyar APC bayan wata ziyara da suka kai masa domin neman mafita kan ƙarancin kuɗin da ake fama da shi waɗanda suka ce hakan na barazana kan ayyukan alkhairi da gwamnatin ta yi.

A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar Malam Garba Shehu ya fitar, Shugaban ya ce sauya fasalin kuɗin da aka yi zai haɓaka tattalin arzikin ƙasar da kuma samar da tagomashi na tsawon lokaci ga ƙasar.

Haka kuma shugaban ya nuna damuwa kan lamuran wasu bankuna a ƙasar inda ya ce kansu kaɗai suka sani kuma a cewarsa ko shekara guda aka ƙara, matsalolin da suke tattare da san kai da zari ba za su gushe ba.
PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp