Home General Hukumar zabe tace a shirye take wajen gudanar da zaben 2023

Hukumar zabe tace a shirye take wajen gudanar da zaben 2023

Shugaban Hukumar Zaben Najeriya Farfesa Mahmood Yakub ya ce za a gudanar da zabukan kasar da ke tafe kamar yadda aka tsara a wannan shekara ta 2023.

Yayin da yake jawabi a taron majalisar zartarwar kasar da Shugaba Muhammadu Buhari ya jagoranta yau Laraba a fadar mulki da ke Abuja, Mahmood ya ce zaben shugaban kasa da ‘yan majalisar tarayya yana nan yadda aka tsara ranar 25 ga watan nan na Fabrairu.

Haka kuma shi ma zaben gwamnoni da na ‘yan majalisar jihohi da za a yi ranar 11 ga watan Maris yana nan ba ja da baya kamar yadda aka tsara yi, in ji shugaban na INEC.

Shugaban hukumar zaben ya bayyana gaban majalisar ne yayin da ya rage kwana 17 a fara zabukan, domin ya yi bayani kan halin da ake ciki game da shirye-shiryen hukumarsa.

Da yake zantawa da manema labarai bayan fitowa daga zauren majalisar, Farfesa Yakubu ya ce ya bayyana ne gaban majalisar ministocin domin sanar da ita irin shirin da hukumar ta yi na gudanar da manyan zabukan na bana.

Ya kara da cewa daman abin da aka saba yi ne a duk lokacin da ake daf da zabe a kasar, shugaban hukumar ya yi wa majalisar zartawa bayani inda shirye-shiryen suka kwana.

Sai dai akwai wasu matsaloli guda uku da a baya hukumar ta ce ka iya yin tarnaki ga gudanar zabukan, matsalolin da suka kunshi rashin tsaro da karancin takardun kudi da kuma man fetur.

Ko baya ga yin wannan bahasin gaban majalisar ministocin, ana sa ran shugaban hukumar zaben ya sake bayyana gaban majalisar magabata ta kasa wato Council of State ranar Juma’a, domin sanar da ita a hukumance irin yadda hukumarsa ta kintsa domin gudanar da manyan zabukan.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp