Home General ASUU ta soki Gwamnatin tarayya bisa Karancin Man Fetur

ASUU ta soki Gwamnatin tarayya bisa Karancin Man Fetur

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta soki gwamnatin tarayya kan ƙarancin Kuɗi da na man fetur da ake fama da shi a faɗin ƙasar.

Wannan na kunshe ta ciki wata sanarwa da shugaban ƙungiyar Emmanuel Osodeke ya fitar ya ce gwamnatin ƙasar a matakan tarayya da jihohi da kuma ƙananan hukumomi na aiwatar da tsare-tsaren da suke wahalar da talakawan ƙasar.

Ya ƙara da cewa matakin da Kotun Ƙolin ƙasar ta ɗauka na dakatar da aiwatar da wa’adin 10 ga watan Fabrairu na daina amfani da tsofaffin takardun kuɗi, zai taimaka wajen sauƙaka wa ‘yan ƙasar halin matsin da suke ciki.

Mista Osodeke ya ƙara da cewa tsarin da gwamnan CBN Godwin Emefiele ya ɓullo da shi na ”hana walwalar kuɗi” an taɓa yin sa a Indiya a shekarar 2016 wanda ya haifar da wahalhalu a ƙasar.

“Dan haka, ASUU tana yaba wa Kotun Ƙoli da wannan hukunci ta hanyar la’akari da halin da talaka ke ciki wanda Emefiele ya jefa su ciki”, in ji Osodeke.

A makon da ya gabata ne dai Kotun Kolin ƙasar ta dakatar da Babban Bankin ƙasar aiwatar da wa’adin 10 ga watan Fabrairu na daina amfani da tsoffin kuɗin, bayan da wasu jihohin ƙasar uku suka shigar da ƙara gaban kotun.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp