Home General Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bayar da umarnin rufe kwalejojin fasaha a faɗin...

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bayar da umarnin rufe kwalejojin fasaha a faɗin ƙasar

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bayar da umarnin rufe kwalejojin fasaha a faɗin ƙasar gabanin babban zaɓen ƙasar da ke tafe ranar 25 ga watan Fabrairu da 11 ga watan Maris da ke tafe.

Ministan Ilimin ƙasar Adamu Adamu ne ya sanar da haka cikin wata wasiƙa da jami’in ma’aikatar I.O Folorunsho ya sanya wa hannu, tare da aike wa babban sakataren hukumar kula da kwalejojin fasaha na ƙasa (NBTE) Idris Bugaje.

Ministan ya umarci shugabannin makarantun duka kwalejojin fasaha cewa a tsadar da karatu daga 22 ga watan Fabrairu zuwa 14 ga watan Maris.

Wasiƙar ta ci gaba da cewa ”Sakamakon fargabar da ake da ita kan tsaron tsaron malamai da ɗalibai da kadarorin makarantunmu, Ministan Ilimi Adamu Adamu bayan tuntuɓa mai zurfi da hukumomin tsaro, ya bayar da umarnin rufe duka makarantun fasahar”

”Dan haka za a rufe makarntun daga ranar Laraba 22 ga watan Fabrairu zuwa 14 ga watan Maris 2023,”

A makon da ya gabata ne dai Hukumar Kula da Jami’o’i ta Najeriya ta bayar umarnin a rufe dukkanin jami’o’in ƙasar tsawon lokacin da za a gudanar da babban zaɓen ƙasar na 2023.

A wata sanarwar mai ɗauke da sa hannun mataimakin shugaban hukumar, mai kula da harkar gudanarwa, Chris J. Maiyaki, ya ce za a rufe jami’o’in ne domin kare lafiyar ma’aikata, da ɗalibai a tsawon lokacin zaɓen.

Bayanin ya ce umurnin ya fito ne daga ministan ilimi na Najeriyar, Adamu Adamu, inda aka umurci dukkanin shugabannin jami’o’i su rufe daga 22 ga watan Fabrairu zuwa 14 ga watan Maris.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp