Home General Sojojin da ‘yan bindiga suka Hallaka a Jamhuriyyar Nijar yanzu haka sun...

Sojojin da ‘yan bindiga suka Hallaka a Jamhuriyyar Nijar yanzu haka sun Kai 17

Adadin sojojin da suka mutu a sakamakon harin kwanton bauna da ‘yan ta’adda su kai musu a jamhuriyar Nijar ya kai 17 kawo yanzu.

Tun farko dai ‘yan ta’addar sun hari sojojin ne a garin Tillaberi dake kudu maso yammacin kasar gab da kan iyakar kasar da Mali, inda nan take suka kashe sojoji 13, wasu 16 kuma suka yi batan dabo.

Ma’aikatar tsaron kasar ta cikin sanarwar da ta fitar, ta ce kawo yanzu an tabbatar da mutuwar sojoji 17, sai wasu 13 da suka jikkata, yayin da har yanzu ake ci gaba da neman guda 12.

Wannan yankin dama ya jima yana fama da ayyukan ‘yan ta’adda, yayin da ayyukan kungiyar Al-Qaeeda da na IS ya ta’azzara musamman daga shekarar 2017.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Abin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina
X whatsapp