Home General NDLEA ta kama muggan ƙwayoyin da aka yi niyyar kai su Turai

NDLEA ta kama muggan ƙwayoyin da aka yi niyyar kai su Turai

Hukumar hana sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Najeriya, NDLEA ta ce ta ƙwace hodar ibilis da tabar wiwi, da wasu muggan ƙwayoyi da aka yi niyyar fitar da su zuwa Turai da wasu sassan na duniya.

A wani saƙo da hukumar ta wallafa a shafinta na Tuwita ta ce ta kama hodar ibilis da nauyinta ya kai kilogram 58, da kuma tabar wiwi a filayen jiragen saman Abuja da Legas da kuma wasu wurare a ƙasar.

Sanarwar ta ce jami’an hukumar sun kama wasu ‘yan kasuwa uku da take zargi da hannu a yankin Ojo da ke Legas

Haka kuma hukumar ta ce ta kwato ƙwayoyin Tramadol miliyan 2,684,900 da wasu magunguna a lokacin samamen da ta gabatar a makon da ya gabata a faɗin ƙasar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Abin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina
X whatsapp