Home General zaben 2023- NRC ta dakatar zirga-zirgar Jiragen kasa a Nijeriya

zaben 2023- NRC ta dakatar zirga-zirgar Jiragen kasa a Nijeriya

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen ƙasa ta Najeriya za ta dakatar da sufurin jiragen ƙasa a faɗin ƙasar na wucin-gadi gabanin babban zaɓen ƙasar da ke tafe.

Wannan na kunshe ta cikin watar  sanarwar da hukumar ta fitar mai ɗauke da sa-hannun mataimakin daraktan yaɗa labarai na hukumar Yakub Mahmood.

sanarwa tace hanyoyin jiragen ƙasan da dakatarwar za ta shafa sun haɗa da Abuja zuwa Kaduna da Warri–Itakpe da Lagos–Ibadan, da kuma hanyar Iddo Lagas-Ijoko.

Haka ta ce ta ɗauki matakin ne domin bayar da dama ga ‘yan ƙasar su gudanar da zaɓukan dake tafe ‘yan kwanaki masu zuwa.

Sanarwar ta kara da cewa Dakatarwar wucin-gadin za ta fara ne daga ranar 25 zuwa 27 ga watan Fabrairun da muke ciki, kamar yadda yake kunshe cikin sanarwar da hukumar ta fitar.

“Haka kuma, hukumar na sanar da al’umma cewa za a maido da zirga-zirgar jiragen ƙasan daga ranar Talata 28 ga watan Fabrairu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Abin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina
X whatsapp