Home General Kotu ta bai wa INEC damar sake saita na’urar BVAS bayan karar...

Kotu ta bai wa INEC damar sake saita na’urar BVAS bayan karar PDP da LP

Kotun daukaka kara a Najeriya ta bai wa hukumar INEC izinin sake saita na’urar zabe ta BVAS da aka yi amfani da ita yayin zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisu da ya gudana a ranar 25 ga watan da ya gabata.

Yayin zaman kotun na ranar laraba a Abuja fadar gwamnatin Najeriya, zaman da ya gudana karkashin jagorancin alkalai 3 da suka hadar da mai shari’a Joseph Ikyegh da ya karanto hukuncin kotun wanda ya sahalewa INEC saita na’urar ta BVAS gabanin zaben gwamnoni da ‘yan Majalisun jihohi da ke tafe a karshen makon nan.

Kotun ta umarci INEC ta nadi bayanan da ke cikin na’urar ta BVAS tare da adana su a waje mai tsaro baya ga sanya kwafi a rumbunan adana bayananta.

Kafin hukuncin na yau dai, Kotu ta baiwa  dan takarar jam’iyyar adawa ta PDP wato Atiku Abubakar da Peter Obi na jam’iyyar LP damar gudanar da bincike kan na’urar da sauran kayakin zabe masu muhimmanci don samun hujjojin da suke ikirarin an tafka magudi a babban zaben kasar.

‘Yan takarar jam’iyyun adawar da suka zo na biyu da na uku a zaben shugaban kasar na Najeriya wanda Bola Ahmed Tinubu ya yi nasara, sun bukaci isa ga na’urorin zaben ne don tattara hujjoji bayan shigar da karar da ke kalubalantar sakamakon zaben shugaban kasar.

Sai dai bayan izinin isa ga na’urorin da kotun sauraren karakin zaben Najeriya ta bai wa ‘yan takarar jam’iyyun adawa, INEC ta daukaka kara kan hukuncin bisa kafa hujjoji da illar da hakan zai yi ga zaben Gwamnoni da ke tafe.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp