Home DUNIYA UNICEF ta koka da karuwar matan da basa samun wadataccen abinci mai...

UNICEF ta koka da karuwar matan da basa samun wadataccen abinci mai gina jiki

Asusun tallafawa kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya koka da karuwar matan da basa samun wadataccen abinci mai gina ciki musamman masu juna biyu da masu shayarwa.

UNICEF cikin wani rahoto da ya fitar ya ce an samu karuwar matsalar da akalla kashi 25 cikin kasashe 13 galibinsu a Afrika da Asiya, tana mai gargadin cewa idan har ba a dauki matakan magance matsalar ba, ko shakka babu za a samu karuwar haifar jarirai masu ciwon yunwa ko kuma Tamow.

Alkaluman da ke kunshe a rahoton na UNICEF ya nuna cewa adadin mata masu juna biyu da masu shayarwa wadanda basa samun abinci mai gina jiki ya karu daga mutum miliyan 5.5 a shekarar 2020 zuwa miliyan 6 da dubu dari 9 a bana.

Rahoton na UNICEF ya alakanta koma bayan da yadda yakin Rasha a Ukraine ya haddasa yunwa musamman a kasashen da suka dogara da ketare ta fannin abinci.

Rahoton na UNICEF ya ce galibin kasashen da wannan matsala ta fi tsananta na sahun wadanda ko dai su ke fama da rikici ko kuma wadanda ‘yan tawaye ko ‘yan ta’adda ke barazana ga tsaronsu.

Cikin jerin kasashen da rahoton ya bayyana a matsayin kan gaba da ke fama da wannan matsala ta yawaitar matan da basa samun abinci mai gina jiki akwai Afghanistan a kan gaba kana Burkina Faso da Chadi da Habasha sannan Kenya da Mali da Nijar sai Najeriya da Somalia tukuna Sudan da Sudan ta kudu sai kuma Yemen.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp