Home Labarai Mayakan kungiyar ISWAP sun kashe masunta 37 a jihar Borno

Mayakan kungiyar ISWAP sun kashe masunta 37 a jihar Borno

Rahotannin na bayyana cewa mayakan kungiyar ISWAP sun kashe masunta 37 a jihar Borno ta arewa maso gabashin Najeriya yayin wani hari da suka kai kansu lokacin da suke tsaka da aiki.

Jagoran mayakan sa kai na jihar Borno Babakura Kolo ya shaidawa AFP cewa ‘yan ta’addan sun farmaki Masuntan ne da ke aikin kamun kifi a wajen kauyen Guggo mai tazarar kilomita 18 daga garin Dikwa tare da kasha mutane 37 ta hanyar harbinsu da kuma jefa gawarwakinsu a ruwa.

Majiyoyi daga yankin sun tabbatarwa kamfanin dillancin labarai na AFP yau alhamis cewa a baya-bayan nan mayakan na ISWAP da takwarorinsu Boko Haram sun tsananta kai hare-hare kan kauyukan jihar ta Borno don satar kayakin abinci.

Mayakan sa kai da ke taimakawa dakarun Sojin Najeriya wajen dakile hare-haren ‘yan ta’adda a yankin sun ce babu tabbaci kan tsagin da ya kai harin na jiya sai dai an tsamo gawarwakin Masuntan 37 a cikin ruwa jiya laraba.

A cewar mayakan, ana ci gaba da laluben gawarwaki a cikin ruwan da kuma cikin dazuka lura da yadda har yanzu aka gaza gano wasu daga cikin Masuntan da suka yi batan dabo.

Rahotanni sun ce mayakan kungiyoyin ‘yan ta’addan na ISWAP da Boko Haram na zargin mazauna kauyukan ko kuma masuntan da sauran manoma da aikin leken asiri ga Sojin Najeriya dalilin da ya sanya kai musu hari.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp