Home Labarai LP ta hade da PDP a jihar Katsina

LP ta hade da PDP a jihar Katsina

Shuwagabannin jam’iyyar Labour Party (LP) reshen jihar Katsina a arewa maso yammacin Najeriya sun amince da marawa dan takarar gwamna karkashin inuwa jam’iyyar PDP a jihar, Sanata Yakubu Dan-marke.

Wakilan jam’iyyar bisa jagorancin mukaddashin shugaban jam’iyyar LP ta jihar, Kwamared Mannir Salisu ya jagoranta, ya ce matakin nasu na zuwa ne bayan shugaban jam’iyyar kuma dan takarar kujerar gwamnan jihar ya dangwarar da shahadar jami’yyar LP zuwa Jam’iyyar APC

A cewar Salisu, ’yan takarar da aka zabo daga unguwanni daban-daban, kananan hukumomi da Jihohi, sun cimma wannan matsayar ne bayan kammala shawarwarin da suka dace da nufin neman sahihin dan takara da zai kai jihar ga tudun mun tsira

Salisu yace ‘ya’yan jam’iyyar da suka fito daga mazabu da dama na jihar sun amince da matakin, haka kuma ya bukaci dukkan magoya bayan jam’iyyar Labour Party dake jihar ta katsina su yi fitar farin dango a ranar 18 ga watan maris su kada kur’aun su ga Jam’iyyar PDP mai alamar laima.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp