Home Labarai NDLEA ta tabbatar da gyara shafinta na daukar aiki

NDLEA ta tabbatar da gyara shafinta na daukar aiki

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta NDLEA ta tabbatawar wa ‘yan Nijeriya dake neman aiki a hukumar cewa ta shawo kan matsalar da ake fuskanta a shafinta na daukar aiki da nufin ganin an sami mafita daga yanzu zuwa ko wanne lokaci.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran hukumar Femi babafemi ya fitar, mai dauke da kwanan wata 15 ga watan Maris 2023. Inda yace sa’oi kadan da bude shafin a ranar lahadi 12 ga wata Maris, ya fara samun tangarda sakamakon yadda mutane sama da dubu 200 ke kokarin cike takardar samun gurbin aiki a hukumar.

Domin warware wannan matsalar hukumar a ranar talata 14 ga watan Maris ta inganta shafin domin daukar dimbin masu bukatar samun gurbin aiki a hakumar bayan da sama da mutane 53,170 suka nasara shiga tashin.

A halin yanzu, shafin yana aiki yadda ya kamata. Don haka hukumar na amfani da wannan dama wajen neman afuwar wadanda suka bibiyi shafin bisa tsaikon da suka samu da su kara hakuri.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp