Home SIYASA Ku dakata da bai wa gwamnatin Kano bashi- Abba Gida-gida

Ku dakata da bai wa gwamnatin Kano bashi- Abba Gida-gida

Sabon zaɓaɓɓen gwamnan jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya shawarci masu bai wa gwamnatin jihar bashi da cewa su dakata.

wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran sabon zaɓaɓɓen gwamnan Sunusi Bature Dawaki Tofa ya fitar, inda tace sabon gwamnan ya shawarci masu bai wa gwamnatin jihar bashi na cikin gida da na waje da kada su amince da bai wa gwamnatin jihar bashi daga ranar 18 ga watan Maris zuwa ranar 29 ga watan Mayu.

Sanarwar ta ci gaba da cewa sabuwar gwamnatin ba za ta yi la’akari da bashin da jihar ta karɓa, ba tare da saninta ba daga ranar zaɓe zuwa ranar da aka rantsar da sabuwar gwamnatin.

Haka kuma sanarwar ta ce masu bin gwamnatin jihar bashi a yanzu su kwana da sanin cewa za a sake nazarin ƙa’idojin bashin bayan kammala bincike a kan kowanne bashi da ake bin jihar.

Ko a makon da ya gabata ma sabon zaɓaɓɓen gwamnan ya bayar da shawara ga masu gine-gine a filayen gwamantin jihar da su dakatar da ayyukansu.

To sai dai ‘yan kwanaki bayan shawarar zaɓaɓɓen gwamnan, gwamnan jihar mai barin gado Abdullahi Umar Ganduje ya mayar masa da martani, yana mai cewa sabon gwamnan ya yi haƙuri, ya daina fitar da sanarwar hukuma da sunan shawara ga jama’a.

duk da cewa ana kallon martanin na Gandujen ka iya zama musayar yawu tsakanin Gwamnatin mai ci da mai barin gado.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp