Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘yan bindiga 5 tare da kwato makamai a jihar Kaduna

Dakarun sojojin Nijeriya runduna ta daya dake aiki a karamar hukumar Chikum a jihar kaduna, sun sami nasarar fatattakar ‘yan bindiga biyar tare da kwato bindigu kirar Ak-7 guda 6 da kuma gidan Alburusai na bindigar AK47 guda shida da kuma wani Alburushi masu tsayin 7.62mm guda 24.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mukaddashin mai Magana da yawun rundunar shiyya ta  daya Lt-Col Musa Yahaya ya fitar a jihar Kaduna.

Yahaya ya bayyana cewa dakarun sun gudanar da atisayen a yankin kan tudun Kaso da kanti zuwa Tantatu a dajin Kubusu dake jihar.

Yace atisayen ya kasance wani bangare na dakile ayyukan ‘yan fashi da masu aikata laifuka domin inganat tsaro da dawo da tattalin arziki mai dorewa a ‘yankin.”

Yahaya ya kara da cewa an fara atisayen ne a tsakar dare juma’a wanda ya sanya ‘yan bindigar suka jigata matuka.

Inda y ace sun sami nasarar kwato Babura hawa guda 3, wayar salula guda biyu da sauran kayayyakin amfani.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 33 minutes 27 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 14 minutes 52 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com