Yan bindiga sun yi garkuwa da Yara sama da 80 a jiharZamfara

wasu rahotanni daga karamar hukumar Tsafe da ke jihar Zamfara a arewa maso yammacin Najeriya sun bayyana cewa ‘yan ta’adda sun yi garkuwa da sama da mutane 80 ne a ranar Juma’a.

Mutanen da lamarin ya ritsa da su daga yankin, bayan isar su daji wajen neman itace da safiyar juma’a, sai labarin sace wasu daga cikin mutanen yankin daga yan bindiga ya kuno kai, a dai dai lokacin da wasu ke cikin aiki a gonakinsu.

Wani mazaunin kauyen Wanzamai da ke karamar hukumar Tsafe a jihar Zamfara mai suna Sani Wanzamai ya ce an yi garkuwa da yara kusan 80 daga kauyen Wanzamai tare da wasu fiye da 20 daga kauyen Kucheri da ke karamar hukumar Tsafe ta jihar da kuma al’ummar Yankara a makwabciyar Katsina. an kuma sace jihar.

Ana sa ran yawan mutanen da yan bindigar suka yi garkuwa da su tsakanin 80 zuwa 100, yawancinsu matasa ne tsakanin shekarun 15-18 da wadanda suka kai shekaru ashirin. Akwai wani dattijo wanda shekarunsa hamsin ne. Sai dai yawancin wandada aka yi awon gaba da su matasa maza da mata ne.

Ya zuwa wannan lokaci ana dakon sanarwa daga rundunar tsaro domin tabbatar da aukuwar wannan al’amari.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 28 minutes 9 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 9 minutes 34 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com