Home Labarai Za a daina ganin dogayen layuka a gidajen mai nan da ƴan...

Za a daina ganin dogayen layuka a gidajen mai nan da ƴan kwanaki – Mele Kyari

Shugaban Kamfanin mai na Najeriya, NNPCL, Mele Kyari ya bayyana fatan cewa layuka a gidajen sayar da mai a fadin kasar zai zama tarihi nan da kwana biyu masu zuwa.

Kyari ya shaida hakan ne a hirarsa da gidan Talabijin na Channels inda ya ce halin da aka shiga ba mai dorewa bane.

A cewarsa, baya tunanin dogayen layukan da ake kafawa zai kai har zuwa ranar Asabar.

Ya bayyana cewa akwai sama da lita miliyan 810 na man fetur a depo-depo da tankoki da kuma gidajen man da ke fadin Najeriya.

A ranar Litinin ne yayin jawabinsa bayan shan rantsuwar kama aiki, sabon shugaban kasa, Bola Tinubu ya ce zamanin biyan tallafin mai ya zo karshe, matakin da ya haifar da tashin farashin man fetur a sassan kasar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp