Home SIYASA Tinubu ya kadu bisa abinda Ganduje ya yiwa kano – Kwankwaso

Tinubu ya kadu bisa abinda Ganduje ya yiwa kano – Kwankwaso

Tsohon gwamnan jihar Kano, Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso, ya ce shugaban kasa Bola Tinubu ne ya gayyaci su, shi da tsohon Gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje kan rushe-rushen da ake yi a jihar.

Kwankwaso, wanda shi ne dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP, ya ce Ganduje a matsayinsa na gwamna ya hana shi daga jihar Kano tsawon shekaru uku da rabi.

Da yake amsa tambayoyi daga manema labaran fadar shugaban kasa, Kwankwaso ya yi ikirarin cewa yawancin gine-ginen da aka rushe gwamnatin Ganduje ce ta sayar da su, ba bisa ka’ida ba, kuma shugaban kasa Tinubu ya kadu a lokacin da ya yi masa bayanin hakikanin abin da yasa ake rushe gine-ginen a halin yanzu.

Da aka tambaye shi ko ya gamsu da sanya bakin da shugaban kasa yayi akan rushe gine-ginen, sai ya ce: “Shugaban ya kadu Shin ba za ku yi mamakin ace muku wani ya sayar da Jami’a ba? Baku yi mamakin yadda ya rusa jami’a ba? Wato Daula Hotel, ga wadanda suka San Kano, ai kun san tsohur Daula, wadda aka rushe, to fa wata tsangaya ce a cikin Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Wudil, shin abun bai baku mamaki ba?” Inji Kwankwaso

“Shugaban kasar ya yi mamaki. Saboda bai sani ba. Ai lokacin Sallar idi ya karato da zaka yi Sallah a filin da kayi takaicin yadda aka mayar da wurin Sallah kasuwa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp