Home DUNIYA Jagoran adawar Kamaru John Fru Ndi ya mutu

Jagoran adawar Kamaru John Fru Ndi ya mutu

Rahotanni daga Kamaru na bayyana cewa Jagoran jam’iyyar adawar kasar ta SDF John Fru Ndi ya mutu a daren litinin ya na da shekaru 81 bayan fama da jinya.

Jagoran adawar shi ne dan siyasa mafi dadewa da ya ci gaba da zama a jam’iyyar adawa tun zuwan siyasar jam’iyyu da dama a kasar.

John wanda ya yi fama da doguwar jinya shi ne dan siyasa daya tilo da ya shafe tsawon lokaci ya na watsi da tayin shugaban kasar Paul Biya wanda ya nemi ya shiga cikin gwamnatin don tafiya tare.

John Fru Ndi ya shafe tsawon shekaru ya na caccakar salon kamun ludayin gwamnatin Paul Biya shugaban da ya shafe shekaru 38 ya na mulkar kasar ta gabashin Afrika.

Zuwa yanzu dai ba a sanar da lokacin gudanar da jana’izar jagoran adawar mai shekaru 81 ba, sai dai tuni ‘yan kasar suka fara makokinsa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp