Kwashe Shara na Kara fito da martabar Kano – Danzago

Gwamnatin jihar Kano ta ce kwashe sharar dake jibge akan titin gidan sarkin Kano daura da gidan Dan masani dab da Kofar shiga Makarantar SAS a matsayin Wani muhimmin aiki Wanda zai Kara fito da martabar Kano.

Shugaban kwamitin karta kwana na kwashe sharar jihar Kano Alhaji Ahmadu Haruna Zago shine ya bayyana hakan a alhamis dinnan lokacin da jami’an hukumar kwashe shara ta jihar suka yi dirar mikiya a wajen domin gabatar da ayyukansu.

A cewar Dan zago hanyar zuwa gidan Dan masani da Kofar shiga Makarantar S.A.S wurare ne masu matukar amfani da tarihi ga al’ummar Kano, a don haka akwai bukatar Samar da kyakkyawan yanayi a wuraren domin samun cikakkiyar tsafta.

Dan zago daga nan sai ya bukaci al’ummar dake rayuwa a yankunan dasu kasance masu bin doka da oda ta hanyar Kai sharar su wuraren da hukuma ta tanada domin zubarwa, wanda hakan zai samar musu da ingantacciyar rayuwa me cike da lafiya da tsafta.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 11 hours 47 minutes 9 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 28 minutes 34 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com