Gwamnatin jihar Kano ta ce kwashe sharar dake jibge akan titin gidan sarkin Kano daura da gidan Dan masani dab da Kofar shiga Makarantar SAS a matsayin Wani muhimmin aiki Wanda zai Kara fito da martabar Kano.
Shugaban kwamitin karta kwana na kwashe sharar jihar Kano Alhaji Ahmadu Haruna Zago shine ya bayyana hakan a alhamis dinnan lokacin da jami’an hukumar kwashe shara ta jihar suka yi dirar mikiya a wajen domin gabatar da ayyukansu.
Read Also:
A cewar Dan zago hanyar zuwa gidan Dan masani da Kofar shiga Makarantar S.A.S wurare ne masu matukar amfani da tarihi ga al’ummar Kano, a don haka akwai bukatar Samar da kyakkyawan yanayi a wuraren domin samun cikakkiyar tsafta.
Dan zago daga nan sai ya bukaci al’ummar dake rayuwa a yankunan dasu kasance masu bin doka da oda ta hanyar Kai sharar su wuraren da hukuma ta tanada domin zubarwa, wanda hakan zai samar musu da ingantacciyar rayuwa me cike da lafiya da tsafta.
PRNigeria hausa
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1190 days 11 hours 47 minutes 9 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 28 minutes 34 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com