Home SIYASA Gwamnan jihar Kano Abba Kabir ya yi sabbin nade-nade

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir ya yi sabbin nade-nade

Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince da nadin shugabannin wasu hukumomi da ma’aikatun gwamnati.

Wannan na kunshe ta cikin wata Sanarwa da babban sakataren yada labaran gwaman, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa PRNigeria.

Wadanda aka nada din sune kamar haka.

1. Injiniya Ado Ibrahim Umar, Manajan Darakta na Kamfanin Wutar Lantarki na Kano (KHEDCO)

2. Alh. Auwalu Mukhtar Bichi, Manajan Daraktan Kamfanin Zuba Jari na kano.

3. Dr. Farouq Kurawa, Manajan Daraktan Hukumar KNARDA.

kafin ba shi wannan mukami , Dakta Kurawa shi ne Babban Sakataren gwamnan Kano wato (PPS) .

4. Dr. Tukur Dayyabu Minjibir, Manajan Daraktan Kamfanin Samar da Taki na Kano (KASCO).

5. Hussain Sarki Aliyu Madobi, Manajan Darakta na Cigaban aiyuka a Kano wato (SKP)

6. Sadiq Kura Muhammad, Manajan Darakta na gidan Zoo Kano (ZGK)

7. Injiniya Sani Bala, Manajan Daraktan Hukumar samar da wutar Lantarki a Karkara (REB)

8. Shamwilu Gezawa, hukumar samar da ruwan sha da tsaftar muhalli ta jihar Kano (RUWASA)

9. Alh. Tukur Bala Sagagi, Manajan Darakta na hukumar yawon bude ido ta jihar Kano

10. Alh. Yahaya Muhammad Idris Manajan Daraktan Kamfanin dab’i na Jihar Kano.

11. Adamu Yahaya, Mataimakin Manajin Darakta (DMD), Kamfanin dab’i na Kano

12. Abba El-mustapha, Sakataren zartarwa na Hukumar Tace Fina-Finai ta Jihar Kano

13. Dr. Muhammad S. Khalil, Babban Sakatare na Hukumar Kula da Sauyin Yanayi ta Jihar Kano (KN-WECCMA).

14. Dr. Dahir M. Hashim, Kodineta na Hukumar Kula da Sauyin yanayi ta Jihar Kano (KN-WECCMA).

Sanarwar na umartar Dukkanin wadanda aka nada dasu karbi ragamar aikin da aka dora musu nan take

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp