Home Labarai Bazoum ya magantu bayan Juyin Mulki a Nijar

Bazoum ya magantu bayan Juyin Mulki a Nijar

Shugaban kasar Nijar Mohamed Bazoum ya yi amfani da kafar sada zumunta ta yanar gizo a ranar alhamis din nan tare da shan alwashin kare dimokiradiyya kwana guda bayan hambarar da shi a wani juyin mulkin da sojoji suka yi.

Ministan harkokin wajen kasar Hassoumi Massoudou shi ma ya fitar da wani rubutu a dandalin X, wanda aka fi sani da Twitter, domin “dukkan masu ra’ayin dimokaradiyya da masu kishin kasa” su sa juyin mulkin ya gaza.

Bayanin nasu ya biyo bayan wani jawabi ne da sojoji suka yi daren ranar Laraba a gidan talabijin na kasar.

Inda suka sanar da cewa an cire Bazoum daga kan karagar mulki tare da dakatar da dukkan hukumomin jamhuriyar, wanda ke zama juyin mulki karo na bakwai a yammacin Afirka da tsakiyar Afirka tun shekara ta 2020.

A ranar Larabar da ta gabata ne jami’an tsaron fadar shugaban kasar suka datse fadar shugaban kasar da ke Yamai babban birnin kasar tare da tare Bazoum a ciki.

Wannan ya haifar da damuwa a yanki da na duniya game da rashin zaman lafiya a kasar da ke zama babbar abokiyar kawance ga kasashen yammacin Turai da ke taimakawa wajen yaki da ta’addanci a yankin Sahel.

Har yanzu ana tsare da Bazoum a cikin fadar shugaban kasa da safiyar Alhamis din nan, Massoudou ya fada a wata hira da kafar yada labaran Faransa ta France 24. Ba a san inda ministan yake ba.

Yamai shiru da sanyin safiyar Alhamis din nan yayin da ‘yan kasar suka farka da rufe kan iyakokin kasar da dokar hana fita da sojoji suka kafa a fadin kasar

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp