Home Labarai Bazoum ya magantu bayan Juyin Mulki a Nijar

Bazoum ya magantu bayan Juyin Mulki a Nijar

Shugaban kasar Nijar Mohamed Bazoum ya yi amfani da kafar sada zumunta ta yanar gizo a ranar alhamis din nan tare da shan alwashin kare dimokiradiyya kwana guda bayan hambarar da shi a wani juyin mulkin da sojoji suka yi.

Ministan harkokin wajen kasar Hassoumi Massoudou shi ma ya fitar da wani rubutu a dandalin X, wanda aka fi sani da Twitter, domin “dukkan masu ra’ayin dimokaradiyya da masu kishin kasa” su sa juyin mulkin ya gaza.

Bayanin nasu ya biyo bayan wani jawabi ne da sojoji suka yi daren ranar Laraba a gidan talabijin na kasar.

Inda suka sanar da cewa an cire Bazoum daga kan karagar mulki tare da dakatar da dukkan hukumomin jamhuriyar, wanda ke zama juyin mulki karo na bakwai a yammacin Afirka da tsakiyar Afirka tun shekara ta 2020.

A ranar Larabar da ta gabata ne jami’an tsaron fadar shugaban kasar suka datse fadar shugaban kasar da ke Yamai babban birnin kasar tare da tare Bazoum a ciki.

Wannan ya haifar da damuwa a yanki da na duniya game da rashin zaman lafiya a kasar da ke zama babbar abokiyar kawance ga kasashen yammacin Turai da ke taimakawa wajen yaki da ta’addanci a yankin Sahel.

Har yanzu ana tsare da Bazoum a cikin fadar shugaban kasa da safiyar Alhamis din nan, Massoudou ya fada a wata hira da kafar yada labaran Faransa ta France 24. Ba a san inda ministan yake ba.

Yamai shiru da sanyin safiyar Alhamis din nan yayin da ‘yan kasar suka farka da rufe kan iyakokin kasar da dokar hana fita da sojoji suka kafa a fadin kasar

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp