Home Labarai Tinubu ya kaddamar da matakan inganta tattalin arzikin

Tinubu ya kaddamar da matakan inganta tattalin arzikin

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayyana kaddamar da wasu matakai daban daban da za su zaburar da tattalin arzikin kasar da zummar shawo kan kuncin rayuwar da jama’ar kasar suka shiga sakamakon cire tallafin man fetur.

‘yan tsiraru kawai ke amfana da shi, yayin da akasarin jama’ar kasar ke shan wahala.

Shugaban ya ce a cikin watanni biyu da suka yi a karagar mulki, gwamnatin sa ta yi nasarar ceto sama da naira triliyan guda daga cikin makudan kudaden da ake zubawa a matsayin tallafin man, wadanda za’a karkatu su wajen bunkasa harkar ilimi da harkokin kula da lafiya da kuma samar da kayan more rayuwa.

Tinubu wanda ya ce ya fahimci halin kuncin da ‘yan Najeriya suke ciki, ya kuma bayyana shirye shirye da dama da gwamnatin sa za ta aiwatar wajen samar da rance ga masu kanana da matsakaitan masana’antu domin bunkasa harkokin su ta yadda za su amfana ta hanyar biyan kashi 9 na kudin ruwa.

Shugaban ya kuma jinjinawa masu kamfanoni da masana’antu saboda dagewar da su ke da ita wajen ci gaba da harkokin su a cikin irin wannan yanayi mai tsauri.

Shugaban Najeriyar Bola Ahmed Tinubu ya ce gwamnatin sa na tattaunawa da kungiyoyin kwadago da zummar kara albashin ma’aikata saboda tinkarar halin da ake ciki, yayin da kuma ya ce zai aiwatar da shirin sa da ya yi alkawari na tallafawa marasa karfi a cikin al’umma

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp