Home Labarai Majalisar Dattijai ta roki kungiyoyin kwadago kan tafiya yajin aiki

Majalisar Dattijai ta roki kungiyoyin kwadago kan tafiya yajin aiki

Ƙungiyoyin ƙwadago sun gabatar da rubutaccen saƙo ga Majalisar Tarayyar Najeriya, a wani ɓangare na zanga-zangar da ta gudanar ranar Laraba.

‘Yan ƙwadagon sun buƙaci shiga tsakanin ‘yan majalisar a dambarwarsu da ɓangaren zartarwa ko kuma su tsunduma yajin aiki a faɗin ƙasar daga ranar Alhamis.

Sai dai mai tsawatarwa, Sanata Ali Ndume, wanda shi ne jagoran kwamitin mutum da majalisar ta wakilta don karɓar masu zanga-zangar da suka je harabar majalisar a Abuja, ya roƙi ‘yan ƙwadagon a kan su jinkirta aniyarsu ta shiga yajin aiki daga Alhamis ɗin nan.

Ya buƙaci ƙungiyoyin ƙwadagon su bai wa Majalisar Tarayyar mako ɗaya a ƙoƙarinta na shiga tsakani don kawo ƙarshen wannan taƙaddama ba tare da durƙusar da harkokin gwamnati da na tattalin arziƙi a ƙasar ba.

Tun da farko, masu zanga-zangar ƙarƙashin jagorancin shugaban NLC babbar ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya, Kwamared Joe Ajero sun yi wa majalisar tsinke cikin rakiyar jami’an tsaro, a yunƙurinsu na ganawa da masu yin dokar.

Sai dai sun gamu da turjiya da farko daga jami’an tsaro, lamarin da ya kai ga karya ƙofar shiga harabar majalisar kuma dandazon masu zanga-zangar suka ɗunguma ciki.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp