Home Labarai Zamu kare Damukradiyya a Nijeriya – Sojojin Nijeriya

Zamu kare Damukradiyya a Nijeriya – Sojojin Nijeriya

Babban hafsan sojin Najeriya Laftanar Janar Taoreed Lagbaja ya ce babban abin da ya fi dacewa da ƙasar a wannan zamani shi ne mulkin dimokradiyya.

Babban hafsan sojin ya bayyana haka ne a lokacin bikin yaye manyan sojoji da aka gudanar da makarantar yaye manyan hafsoshi ta Jaji da ke Kaduna, kamar yadda wata sanarwa da kakakin rundunar Burgediya Janar Onyema Nwachukwu ya fitar.

Laftanar Janar Lagbaja ya ce dole ne a tunasar da sojojin ƙasar cewa taimakonsu wajen tabbatuwa da ɗorewar mulki shi ne babbar hanyar nuna ƙwarewa a aikin soji.

Ya kuma ce babban burin kowanne ɗan Najeriya a yanzu shi ne ɗorewar mulkin dimokradiyya, wanda zai tabbatar da haɗin kan ƙasa da kuma kare muradun ‘yan Najeriya, ba tare da la’akari da bambanci addini ko na ƙabila ba.

”A don haka ina kira ga duka sojojin Najeriya su bayar da gudunmowarsu wajen tabbatar da ɗorewar mulkin dimokraɗiyya, sannan su kauce wa shiga lamuran siyasa a lokacin gudanar da ayyukansu”, in babban hafsan sojojin.

Ya kuma jaddada burin rundunar sojin ƙasar na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin ƙasar.

Laftanar Janar Lagbaja ya ce sojojin ƙasar tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaron ƙasar na aiki ba dare ba rana domin tabbatar da kare martabar ƙasar.

Babban hafsan sojin na wannan jawabi ne a daidai lokacin da ƙasashen ƙungiyar Ecowas suka bai wa sojojin da suka hamɓarar da gwamnatin farar hula ta Mohamed Bazoum a Nijar wa’adin mako guda na su mayar da shi kan mulki su fuskanci tarin takunkumai, ciki har da na matakin Soji.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp