Home SIYASA Atiku ya zargi hukunci kotu da cire yadda ga ‘yan Nijeriya

Atiku ya zargi hukunci kotu da cire yadda ga ‘yan Nijeriya

Jagoran adawar Najeriya, ya nemi gaggauta yi wa tsarin mulkin ƙasar gyaran fuska, don hana kotuna abin da ya kira “fakewa a bayan gaza bin ƙa’idojin shigar da ƙara da muhawarorin shari’a masu rikitarwa, suna tabbatar da zaɓen sata da kuma yin zagon ƙasa ga zaɓen al’umma”.

Atiku Abubakar ya ce wajibi ne a mayar da zaɓe da tattara sakamako ta hanyar laturoni, su zama tilas a Najeriya.

Wannan, wani ɓangare ne na taron manema labarai da shugaban adawar, kuma ɗan takarar jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, ya gabatar ranar Litinin a Abuja. Taron na zuwa ne kwana uku, bayan hukuncin kotun ƙoli da ya yi watsi da ƙararsa ta ƙalubalantar nasarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Kotun dai ta yi watsi da ƙararrakin da Atiku Abubakar tare da takwaransa na jam’iyyar LP, Peter Obi suka ɗaukaka, inda ta ce ba su da ƙwararan hujjoji.

Atiku ya ce matsayin Kotun Kolin ko da yake, shi ne ƙarshe, amma dai ya bar baya da ƙura mai yawa.

Ya yi zargin cewa hukunce-hukuncen kotunan zaɓe, sun zaizaye yardar da ‘yan Najeriya ke da ita, ga tsarin zaɓe da kuma dimokraɗiyyar Najeriya.

Ya ce yana mamakin wanda zai shawo kan miliyoyin ‘yan Najeriya, su fita su yi zaɓe nan gaba, bayan sun bi layi sun yi rijista bisa tabbacin da INEC ta ba su, amma sai suka ga an sace ƙuri’unsu, tare da bai wa waɗanda ba su zaɓa ba, nasara.

Dan adawan ya ce idan mutane suka daina yarda, kuma suka dawo daga rakiyar zaɓuka, dimokraɗiyya ta durƙushe ke nan. Kuma ta hanyar tabbatarwa da halasta ci gaba da rashin gaskiya a zaɓuka, kotunan Najeriya, na ƙwace ‘yancin masu zaɓe, na zaɓar wa kansu shugabanni.

Ita dai hukumar zaɓe ta ce ta yi zaɓe cikin gaskiya da adalci, kuma sakamakon hukunce-hukunce da aka yanke a kotuna sun nuna cewa INEC ta taka rawar gani.

PRNigeria haus

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp