Home SIYASA Atiku ya zargi hukunci kotu da cire yadda ga ‘yan Nijeriya

Atiku ya zargi hukunci kotu da cire yadda ga ‘yan Nijeriya

Jagoran adawar Najeriya, ya nemi gaggauta yi wa tsarin mulkin ƙasar gyaran fuska, don hana kotuna abin da ya kira “fakewa a bayan gaza bin ƙa’idojin shigar da ƙara da muhawarorin shari’a masu rikitarwa, suna tabbatar da zaɓen sata da kuma yin zagon ƙasa ga zaɓen al’umma”.

Atiku Abubakar ya ce wajibi ne a mayar da zaɓe da tattara sakamako ta hanyar laturoni, su zama tilas a Najeriya.

Wannan, wani ɓangare ne na taron manema labarai da shugaban adawar, kuma ɗan takarar jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, ya gabatar ranar Litinin a Abuja. Taron na zuwa ne kwana uku, bayan hukuncin kotun ƙoli da ya yi watsi da ƙararsa ta ƙalubalantar nasarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Kotun dai ta yi watsi da ƙararrakin da Atiku Abubakar tare da takwaransa na jam’iyyar LP, Peter Obi suka ɗaukaka, inda ta ce ba su da ƙwararan hujjoji.

Atiku ya ce matsayin Kotun Kolin ko da yake, shi ne ƙarshe, amma dai ya bar baya da ƙura mai yawa.

Ya yi zargin cewa hukunce-hukuncen kotunan zaɓe, sun zaizaye yardar da ‘yan Najeriya ke da ita, ga tsarin zaɓe da kuma dimokraɗiyyar Najeriya.

Ya ce yana mamakin wanda zai shawo kan miliyoyin ‘yan Najeriya, su fita su yi zaɓe nan gaba, bayan sun bi layi sun yi rijista bisa tabbacin da INEC ta ba su, amma sai suka ga an sace ƙuri’unsu, tare da bai wa waɗanda ba su zaɓa ba, nasara.

Dan adawan ya ce idan mutane suka daina yarda, kuma suka dawo daga rakiyar zaɓuka, dimokraɗiyya ta durƙushe ke nan. Kuma ta hanyar tabbatarwa da halasta ci gaba da rashin gaskiya a zaɓuka, kotunan Najeriya, na ƙwace ‘yancin masu zaɓe, na zaɓar wa kansu shugabanni.

Ita dai hukumar zaɓe ta ce ta yi zaɓe cikin gaskiya da adalci, kuma sakamakon hukunce-hukunce da aka yanke a kotuna sun nuna cewa INEC ta taka rawar gani.

PRNigeria haus

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp