Home Labarai Tinubu ya bukaci majalisar wakilai ta amincewa da kasafin tiriliyan 2.1

Tinubu ya bukaci majalisar wakilai ta amincewa da kasafin tiriliyan 2.1

Hoton Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya rubutawa majalisar wajilan Nijeriya wasika kan su amince da kwarya-kwaryar kasafin kudi na naira tiriliyan 2.1 domin kara albashin ma’aikata da kuma wasu sabgogi tsaro da sauransu.

Haka kuma shugaban ya aikewa majalisar da tsarin kasha matsakaici na tsakanin shekarar 2024-2026 zuwa ga majalisar.

A ranar litinin, majalisar zartarwa ta tarayya (FEC) ta amince da Karin kasafin kudin shekarar 2023 na  naira tiriliyan 2.1.

Yayin da yake ganawa da manema labarai jim kadan bayan fitowa daga taron  majalisar ta tattalin arzikin a Abuja, ministan kasafi da tsare-tsare, Atiku Bagudu, yace an amince da kasafin ne domin magance wasu lamurran kudi na gaggawa

Ministan ya bayyana cewa “Majalisar ta amince da kwarya-kwaryar kasafin da aka bukata matsayin kasha na biyu a shekarar 2023,”.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp