Home Labarai Jirgin sojin saman Nijeriya ya yi hadari

Jirgin sojin saman Nijeriya ya yi hadari

Nigeria Airforce

Wani helikwaftan rundunar sojojin saman Najeriya ya yi hatsari a Fatakwal, babban birnin jihar Ribas da safiyar yau Juma’a.

Mai magana da yawun rundunar, Edward Gabkwet ne, ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar.

Ya ce dukkan wadanda ke cikin jirgin sun kubuta, ko da yake sun samu “kananan raunuka”.

Jirgin helikwaftan kirar MI-35P ya yi hatsari ne da misalin karfe 7.45 na safe, jim kadan bayan ya tashi a kan hanyarsa ta zuwa yaki da masu zangon ƙasa ga tattalin arzikin kasa da ke fasasa bututu suna satar man fetur a jihar Ribas.

“Abin farin cikin shi ne dukkan ma’aikatan jirgin 5 sun kubuta da rayukansu, sai dai kananan raunuka kuma a halin yanzu ana kula da su a wani asibitin sojoji da ke Fatakwal.

“Babban hafsan sojojin sama, Air Marshal Hassan Abubakar, a halin yanzu yana kan hanyarsa ta zuwa Fatakwal, don ganin halin da ake ciki da kansa, kuma da niyyar duba lafiyar ma’aikata,” in ji sanarwar.

ana ganin yawaitar hatsari da jiragen saman sojin Najeriya ke yi wanda ke janyo asarar rayuka, ya zama abin damuwa matuƙa a cikin shekara biyu, inda masu ruwa da tsaki suka yi kira ga sojoji, su kiyaye hanyoyin gudanar da ayyukansu da kuma kula da jiragensu na yau da kullum.

A watan Agustan 2023 ma, jirgin saman sojin Najeriya NAF MI-171 ya yi hatsari a kusa da kauyen Chukuba na jihar Neja, inda ya haddasa asarar sojoji.

A 2021, sojoji akalla 20 ne suka rasu cikin wata uku a hadurra uku na jiragen saman sojin Najeriya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp