‘Yan sandan Sun hallaka ‘yan bindiga 50 a Jihar Taraba

rahotannin daga Nijeriya na bayyana cewa an hallaka ‘yan bindiga fiye da 50 da ake zargin su ne ke addabar karamar hukumar Bali ta Jihar Taraba.

Rundunar ƴan sanda a jihar ce ta bayyana haka ta bakin Kakakin ta Abdullahi Usman ta shaida hakan a ranar Alhamis cewa jami’an ‘yan sanda tare da hadin gwiwar wasu jami’an tsaro ne suka kashe ‘yan fashin dajin.

Ya ce aikin hadin gwiwar ya zo ne bayan korafe-korafe da mutanen yankin suka yi wanda ya kai ga yi wa ƴan fashin kwanton bauna tare da halaka  su.

“Rundunar ‘yan sandan jihar Taraba ta samu labarin cewa wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wane ne ba, amma dai ana zargin masu garkuwa da mutane ne, daruruwan su sun kai farmaki kauyen Tonti da ke karkashin gundumar Maihula cikin karamar hukumar Bali a jihar Taraba.

“‘Yan bindigan sun kai farmaki kauyen ne da misalin karfe 5:30, kuma suka fara harbe-harbe,” kamar yadda ya shaida wa Channels.

“Da samun bayanai, kwamishinan ‘yan sandan Taraba, Joseph Eribo, ya bayar da umarnin tura wata zugar jami’an tsaro daga reshen Bali zuwa yankin ciki har da hadin gwiwar sojoji da ‘yan banga, da mafarauta.”

Ya ce suna ci gaba da farautar ‘yan ta’addan da suka tsere, kuma an tura wata runduna ta musamman domin inganta tsaro a yankin.

Sai dai ya kara da cewa: “Wani abin takaici shi ne ‘yan bindigan sun harbe mutanen yankin 12 kafin jami’an tsaro su isa”.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 23 hours 36 minutes 37 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1173 days 1 hour 18 minutes 2 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com