shugaban hukumar NAHCON ya bukaci a rage kudin Hajjin bana.

Mukaddashin shugaban hukumar NAHCON, Malam Jalal Ahmad Arabi, ya bukaci hukumomin jin dadin Alhazai na jihohin Nijeriya da su yi dukkan mai yiwuwa wajen ganin sun rage kudin hajjin shekarar 2024.

ya bayyana hakan ne ranar Alhamis yayin da yake karbar bakuncin sakatarori da shuwagabannin, da kuma shuwagabannin sojojin Nijeriya a shalkwatar hukumar dake birnin tarayya Abuja.

haka kuma ya bukaci su dasu sanya kudin da suka karba zuwa yanzu a asusun hukumar ta NAHCON, domin adadin kudin su zasu bayyana mataki na gaba da za’a dauka.

“babu lokaci, ya kamata ku sanya kudin da kuka karba a Asusun NAHCON, domin yin shirye 0 shiryen farko kafin aikin Hajjin, gami da ziyara domin kulla alaka da ayyukan da za’a gudanar a yayin aikin hajjin.

“ta yadda mutanen mu zasu gansu da kokarin mu da nasarorin da zamu samu sakamakon shirin da mukayi don aikin hajjin shekarar 2024 ya zo cikin sauki,” a cewar sa.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 18 hours 7 minutes 49 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 19 hours 49 minutes 14 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com