Home Labarai Tinubu ya kadu bisa rasuwar Akeredolu

Tinubu ya kadu bisa rasuwar Akeredolu

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa yana cikin alhini tare da al’ummar jihar Ondo, bisa rasuwar gwamnansu, Rotimi Akeredolu.

A cikin wata wasiƙa da ya fitar, Tinubu ya ce “Ba za mu sake ganin mutum kamarsa ba”.

Ya ce gwamnatinsa za ta karrama Gwamna Rotimi don ganin ba a mance da hidimar da ya yi wa al’umma ba.

Tinubu ya ce tuni ya yi wayar tarho da uwargidan marigayin Betty da kuma mai riƙon muƙamin gwamnan jihar Lucky Aiyedatiwa inda ya miƙa ta’aziyyarsa gare su kan wannan rashi.

Ya bayyana Gwamna Akeredolu ba kawai a matsayin aboki ba, ɗan’uwansa ne kuma shaƙiƙi. Ya bayyana mutuwar a matsayin babban rashi ga jam’iyyarsu ta APC mai mulki da kuma iyalai ma’abota rajin ci gaba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp