Home Labarai Tinubu ya kadu bisa rasuwar Akeredolu

Tinubu ya kadu bisa rasuwar Akeredolu

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa yana cikin alhini tare da al’ummar jihar Ondo, bisa rasuwar gwamnansu, Rotimi Akeredolu.

A cikin wata wasiƙa da ya fitar, Tinubu ya ce “Ba za mu sake ganin mutum kamarsa ba”.

Ya ce gwamnatinsa za ta karrama Gwamna Rotimi don ganin ba a mance da hidimar da ya yi wa al’umma ba.

Tinubu ya ce tuni ya yi wayar tarho da uwargidan marigayin Betty da kuma mai riƙon muƙamin gwamnan jihar Lucky Aiyedatiwa inda ya miƙa ta’aziyyarsa gare su kan wannan rashi.

Ya bayyana Gwamna Akeredolu ba kawai a matsayin aboki ba, ɗan’uwansa ne kuma shaƙiƙi. Ya bayyana mutuwar a matsayin babban rashi ga jam’iyyarsu ta APC mai mulki da kuma iyalai ma’abota rajin ci gaba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp