Home Labarai Tinubu ya kadu bisa rasuwar Akeredolu

Tinubu ya kadu bisa rasuwar Akeredolu

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa yana cikin alhini tare da al’ummar jihar Ondo, bisa rasuwar gwamnansu, Rotimi Akeredolu.

A cikin wata wasiƙa da ya fitar, Tinubu ya ce “Ba za mu sake ganin mutum kamarsa ba”.

Ya ce gwamnatinsa za ta karrama Gwamna Rotimi don ganin ba a mance da hidimar da ya yi wa al’umma ba.

Tinubu ya ce tuni ya yi wayar tarho da uwargidan marigayin Betty da kuma mai riƙon muƙamin gwamnan jihar Lucky Aiyedatiwa inda ya miƙa ta’aziyyarsa gare su kan wannan rashi.

Ya bayyana Gwamna Akeredolu ba kawai a matsayin aboki ba, ɗan’uwansa ne kuma shaƙiƙi. Ya bayyana mutuwar a matsayin babban rashi ga jam’iyyarsu ta APC mai mulki da kuma iyalai ma’abota rajin ci gaba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp