Home Labarai Sojoji sun hallaka jagoran ISWAP a jihar Borno

Sojoji sun hallaka jagoran ISWAP a jihar Borno

Dakarun sojin saman Nijeriya sun sami nasarar hallaka jagoran mayakan ISWAP Ba’a Shuwa a jihar Borno.

Harin na ranar talata yayi sanadiyar mutuwar mayakan na ISWAP da dama sun.
Zagazola Makama mai bincike kan lamurran da suka shafi tsaro a yankin tafkin Chadi, ya ruwaito cewa harin da yayi sanadiyar Shuwa ya auku ne a Kwatan Dilla, dake karamar hukumar Abadam ta jihar Borno.

Yace hotuna sun nuna yadda gawarwakin mayakan da aka hallaka ke kwance.
Mayakan dai na boye a wata maboyar su domin gujewa luguden wuta da sojojin ke yi a yankin Timbuktu triangle.

Shuwa ya zama jagoran ISWAP a shekarar 2021, bayan mutuwar Abubakar Shekau.
Haka Kuma ya jagoranci gudanar da ayyukan ta’addanci Chiralia, Markas Kauwa, Abirma, Buk, Abulam, Dusula, Abbagajiri, Gorgore da sauran yankuna da dama na Timbuktu da Alagarno a jihar Borno.

Shuwa da tawagar sa na da alhakin hare-haren bama bamai a garuruwan Damaturu-Maiduguri, Askira, Buratai, Buni Yadi, Buni Gari, Gaidam da sauran yankunan dake jihohin Borno da Yobe.

PRNigeria hausa

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp