Home Labarai Tinubu Ya gana da Hafsoshin tsaron Kasar kan matsalar Tsaro

Tinubu Ya gana da Hafsoshin tsaron Kasar kan matsalar Tsaro

Shugaban Nijeriya Asiwajo Bola Tinubu ya gana da hafsoshin tsaron kasar da kuma wasu manyan hukumomin tsaro a fadarsa da ke birnin tarayya Abuja, a ranar Talata.

Hafsoshin tsaron da suka halarci ganawar sun haɗa da babban hafsan tsaro, Janar Christopher Musa, shugaban rundunar sojin ƙasa, Laftanar-Janar Taoreed Lagbaja, shugaban sojin sama, Air Marshal Hassan Abubakar, da kuma shugaban sojojin ruwa, Vice Admiral Emmanuel Ogalla.

haka kuma mai taimakawa shugaban ƙasa kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu na cikin waɗanda suka halarci taron.

Sun tattauna kan batun karuwar aikata ta’addanci, garkuwa da mutane da kuma kashe-kashe a faɗin kasar da nufin magance su.

Nijeriya dai na guda cikin kasashen yammacin Afirka dake fama da matsalar rashin tsaro, kama daga masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa dake cin karensu babu babbaka a yankin Arewa maso yamma da wasu jihohi a tsakiyar kasar.

sai kuma mayakan boko haram da na ISWAP dake tayar da kayar baya a yakin arewa maso Gabas, sai Kudu maso kudu da wasu yankuna a kudancin kasar dake fama da mayakan IPOB masu rajin kafa kasar Biyafara.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp