Home General Mun Kama ‘Yan dabar da Wani Dan Siyasa ya tura ƙunci da...

Mun Kama ‘Yan dabar da Wani Dan Siyasa ya tura ƙunci da Tsanyawa – CP Gumel.

Rundunar ‘yan Sandan Kano ta tabbatar da kama wasu ‘yan Daba, da ake zargin wani Dan Siyasa ya tura wurin Zaɓen cike gurbi ,na ƙananan Hukumomin ƙunci da Tsanyawa.

Kwamishinan ‘Yan Sandan kano CP. Muhammad Hussaini Gumel ne ya bayyana hakan, Jim kadan da kama gungun matasan a lokacin da suke zagayen yadda Zaɓen cike gurbin yake gudana.

CP Gumel ya ƙara da cewa, tuni ‘Yan daban suka kama sunan ɗan Siyasa me Suna Gwarmai, a matsayin Wanda ya turo su domin su je su tayar da hankali a wurin Zaɓen cike gurbin na Ƙunci da Tsanyawa.

‘Yan Sandan sun kama ‘yan dabar da makamai ne, samfurin Adduna, Gorori, Gariyo, da dai sauran su, a dai-dai lokacin da suke kan hanyar su ta shiga garin Ƙunci.

Gumel yace zasu Binciki Dan Siyasar domin tabbatar da gaskiyar lamarin dama gurfanar dashi a gaban kuliya, matukar zargin yayi ƙarfi a kansa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp