Home Labarai Ya kamata a cire tallafin wutar Lantarki a Nijeriya – IMF

Ya kamata a cire tallafin wutar Lantarki a Nijeriya – IMF

Asusun Bada Lamuni na Duniya IMF, ya shawarci gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu, da ta cire tallafin lantarki gaba daya, duk da cewa ‘yan kasar na kokawa da tsadar rayuwa, bayan tallafin mai da gwamnatin ta cire a watan Mayun 2023.

A cewar wani rahoto da IMF ya wallafa a shafinsa na yanar gizo, yace gwamnatin Najeriya tana tursasa kanta kan abubuwan da suka neman fin karfinta, don haka akwai bukatar ta janye tallafin lantarki kamar yadda ta cire na man fetur.

Cibiyar ta Bretton Woods ta bayar da wannan shawarar a matsayin hanyar da Najeriya za ta bi domin farfado da tattalin arzikin kasar da ya shiga wani hali, abin da ke zuwa daidai lokacin da gwamnatin kasar ta ce tallafin wutar lantarki tsakanin watan Janairu zuwa Satumban 2023 ya lakume Naira biliyan 375.8, yayin da masu amfani da wutar lantarki suka biya jimillar naira biliyan 782.6.

IMF ya yabawa gwamnatin Najeriya kan sauye-sauyen da ta aiwatar zuwa yanzu amma ta sake nanata cewa ya kamata a cire tallafin lantarki kamar yadda aka cire a bangaren man fetur.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp