Home Labarai Gwamnatin Nijeriya ta bayyana wadanda karin kudin lantarki ya shafa

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana wadanda karin kudin lantarki ya shafa

Hukumar kula da wutar lantarki a Najeriya ta amince da ƙara kuɗin wuta ga aboka hulɗarsu da ke ajin Band A – masu samun wuta tsawon sa’a 20 a rana.

Mataimakin shugaban hukumar, Musuliu Oseni ya bayyana cewa a yanzu kwastamomin za su biya N225 kan kowane kilowatt inda a baya suke biyan N66.

A taron manema labarai da aka yi a Abuja ranar Laraba, Oseni ya ce abokan hulɗarsa da ke samun wuta tsawon sa’a 20 a rana sune kashi 15 cikin 100 na kwastamomin hukumar a Najeriya.

Ya ƙara da cewa hukumar ta kuma sauke kwastamomin da ke ajin Band A zuwa Band B masu samun wuta ƙasa da sa’a 20 a rana saboda rashin kamfanonin rarraba hasken wutar lantarki na basu wutar da ta kamata.

Ya bayyana cewa ƙarin ba zai shafi kwastamomin da ke sauran matakan ba.

Tun bayan samun bayanai cewa hukumomi na iya ƙara kuɗin wuta ne, al’ummar Najeriya ke ta martani a shafukan sada zumunta inda wasu ke ganin matakin ya zo a lokacin da jama’a ke fama da tsadar rayuwa da kuma rashin tsayayyiyar wutar lantarki da ake fuskanta.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp