Home Labarai Gwamnatin Nijeriya ta bayyana wadanda karin kudin lantarki ya shafa

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana wadanda karin kudin lantarki ya shafa

Hukumar kula da wutar lantarki a Najeriya ta amince da ƙara kuɗin wuta ga aboka hulɗarsu da ke ajin Band A – masu samun wuta tsawon sa’a 20 a rana.

Mataimakin shugaban hukumar, Musuliu Oseni ya bayyana cewa a yanzu kwastamomin za su biya N225 kan kowane kilowatt inda a baya suke biyan N66.

A taron manema labarai da aka yi a Abuja ranar Laraba, Oseni ya ce abokan hulɗarsa da ke samun wuta tsawon sa’a 20 a rana sune kashi 15 cikin 100 na kwastamomin hukumar a Najeriya.

Ya ƙara da cewa hukumar ta kuma sauke kwastamomin da ke ajin Band A zuwa Band B masu samun wuta ƙasa da sa’a 20 a rana saboda rashin kamfanonin rarraba hasken wutar lantarki na basu wutar da ta kamata.

Ya bayyana cewa ƙarin ba zai shafi kwastamomin da ke sauran matakan ba.

Tun bayan samun bayanai cewa hukumomi na iya ƙara kuɗin wuta ne, al’ummar Najeriya ke ta martani a shafukan sada zumunta inda wasu ke ganin matakin ya zo a lokacin da jama’a ke fama da tsadar rayuwa da kuma rashin tsayayyiyar wutar lantarki da ake fuskanta.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp